Ziyara ga Buhari : Mimiko ya bayyana dalilin zuwansa
– Gwamna Mimiko yace dalilinsa na kaiwa ziyara shine domin tabbatar da gaskiya akan rikicin jihar Ondo
– Wannan na zuwa ne mako daya bayan Mimiko ya kaiwa Buhari ziyara a fadar sa
– Yace zalunci ne canza sunan Eyitayo Jegede da Jimoh Ibrahim
Gwamnan jihar Ondo , Olusegun mimiko yace ba ya shirin shekewa daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC.
Ya musanta maganan cewa ya kaiwa shugaba Buhari ziyara ne saboda shekewa zuwa jam’iyyar APC, Vanguard ta bada rahoto.
Mimiko ya bayyana hakan ne yayinda yake Magana da mane,a labarai a Akure, ranan 6 ga watan Numwamba ,bayan ganawa da masu ruwa da tsakin jam’iyyar na kananan hukumomi 18 na jihar.
KU KARANTA: Buhari ya maida wadanda suka gama jami’a ‘yan kamasho – Kakakin Jonathan
Yace daya daga cikin dalilansa na zuwa wurin Buhari shine bisa ga rashi adalcin da akayi akan canjin sunan dan takaran jam’iyyar karkashin PDP.
Ya ce ya je rokon shugaba Buhari ne a matsayinsa na shugaban kasa domin tabbatar da adalci.
Game da cewar sa, Buhari yayi alkawarin cewa za’a tabbatar da adalci akan abun,
Mimiko said: “ What happened with the substitution was a contrived conspiracy because the decision of INEC cannot find comfort in Justice, principle, law, and morality.”
Mimiko yace: “Abinda ya faru da canjin shine wata kullaliya ce saboda INEC ta kasa yin adalci da abinda ya kamata.”
The post Ziyara ga Buhari : Mimiko ya bayyana dalilin zuwansa appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read Naij.com 24/7.