Akwai yiyuwar Najeriya ta fara ciyar da kanta abinci – Biyora
– Wani matashi dayayi wani rubutu a shafin Facebook ya bayyana cewa akwai yiyuwar Najeriya ta fara dogara da kanta akan abinci a wannan shekarar
– Rabiu Biyora yayi godiya ga shugaban kasa Muhammadu Buhari
– Mutane sun maganta inda suka amince dashi
Rabiu Biyora a cikin gona
Gonar
Wani matashi mai suna abiu Biyora a shafin facebook yayi godiya ga shugaban kasa Bhari akan irin tallafin da yake bawa harkokin Noma inda ya bayyana cewa, masana sunyi hasashe cewa akwai yiyuwar Najeriya ta fara dogara da kanta daga wannan shekarar.
KU KARANTA: Buhari ya yaba ma sojojin Najeriya
Biyora kuma ya saki wasu hotuna inda suka nuna shi a cikin wata katuwar Gona tare da wasu mutane inda suke yima gonar feshi. Mutane da yawa sun maganta akan rubutun nashi inda suka nuna jin dadin su kuma sukayi godiya da addu’a da shugaban kasa Muhammadu Buhari.Noma nada matukar muhimmanci a Najeriya inda sama da kashi 60 na Najeriya suna harkar noma, kuma yana daya daga cikin sana’o’in da aka yadda ma’aikatan gwamnati suyi alhali suna aiki.
Biyora da abokan sh
A lokacin yakin neman zabe, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sha alwashin tallafawa harkokin noma domin Najeriya ta cinma dogaro da kanta. A watan 2 da suka wuce ne shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bada umurni cewa a bude ma’ajiyoyi na abinci na gwamnati domin a samar da saukin abinci da ya tsananta. Domin kuwa hukumar Kastam ta dakatar da shigowa da shinkafa ta haramtacciyar hanya.
A wani labarin kuma, gwamnatin tarayyar Najeriya ta bawa ma’aikata hutu a ranakun Talata da Laraba domin a gudanar da bukuwan Sallah. Wannan yazo ne daga ofishin Ministan cikin gida, Janar Abdurrahman Danbazau inda suka bayar da sanarwar a yau.
The post Akwai yiyuwar Najeriya ta fara ciyar da kanta abinci – Biyora appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Nigerian newspapers 24/7.