Minista ya bai wa yan NYSC lambar yabo
Minista ya bai wa wadanda suka yi ma Kasa hidima lambar yabo
– Mutane 76 da suka yi aikin hidimar Kasa (Watau NYSC) sun samu lambar yabo daga wajen Ministan Tarayyar Abuja, Malam Muhammad Musa Bello
– An bada lambar yabon ne ga wadanda suka yi aikin hidimar Kasar a Birnin Tarayyar Abuja daga Shekarar 2011 zuwa 2013
– Ministan yace za a cigaba da bada irin wannan kyauta ga duk mai bautar Kasar da yayi wani aikin taimakon al’umma
Mutane 76 wadanda suka yi ma kasa bauta (NYSC) a babban Birnin Tarayyar Najeriya, Abuja daga Shekarar 2011 zuwa Shekarar 2013 sun samu karbar kyauta daga Ministan Harkokin Birnin Tarayyar Malam Muhammad Bello. Malam Muhammad Musa Bellon ya bayyana hakan wajen taron rufe kwas din bitar da aka gabatarwa masu bautar Kasar na wannan Shekarar a Garin Kubwa. Minastan har wa yau yace za su baiwa wadanda suka yi aikin azo-a-gani a shekarar 2014 har zuwa bana irin wannan lambar yabo. Babban Sakataren ma’aikatar Tarayyar, Dr. Babatope Ajakaiye ya wakilci ministan a taron, ya sanar da cewa Gwamnatin Birnin Tarayyar za ta cigaba da bada lambar yabo ga duk dan bautar Kasar da ya zo yayi abin a zo gani. Ministan yace: “Akwai bukatar ku san cewa mun shirya bada kyautar lamban yabo ga mutane 76 wadanda suka yi abin da ba za a manta ba yayin yi ma Kasar su hidima a wannan gari daga shekarar 2011 zuwa 2013, muna sa ran bada wasu kyatuttukan ga wadanda suka yi bautar Kasar su daga shekara ta 2014 zuwa Shekarun yau.”
KU KARANTA: KUNGIYAR IPOB TAYI TIR DA TSAGERUN NIGER DELTA AVENGERS
A baya dai, Daraktan NYSC din Birgediya-Janar Sule Kazaure ya bada shawara ga masu bautan Kasar da su auri ‘Yan uwan su da suka fito daga kabila dabam. Ya bada wannan shawara ne ga masu bautar Kasan na wannan shekara ta 2016 lokacin da ya kai ziyara a sansanen su da ke Kubwa, Birnin Abuja. Cewar Birgediya-Janar Kazaure, yin hakan shi zai kara dankon hadin-kai a Kasar ta Najeriya. Tuni ma dai amfanin tsarin na NYSC shine a kara hadin-kan ‘yan Kasa baki daya.
The post Minista ya bai wa yan NYSC lambar yabo appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Nigerian newspapers 24/7.