Aisha Buhari ta gama ziyararta na kasar Amurka, zata dawo Najeriya (Hotuna)
Matar shugaban kasa Muhammadu Buhari Aisha, ta gama ziyarar kwanaki hudu da ta kai kasar Amurka ta kuma isa kasar Landan a hanyarta na dawowa gida Najeriya
Jami’an kasar Amurka sun raka matar shugaban kasa Buhari, Aisha tare da yarta Zahra masauki yayin da take kokarin hawa jirgin zuwa kasar Landan.
Matar shugaban kasar Najeriya, Aisha Buhari ta isa kasar Landan a hanyar ta na dawowa bayan ta kammala abunda ya kai ta kasar Amurka.
A daidai wannan lokacin, jam’iyyar Peoples Democratic Party babin Jihar Ekiti sunce tafiyar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari da ake ta yayatawa, tafiya ne da ya kamata yan Najeriya su yi suka a kai.
KU KARANTA KUMA: Yadda Buhari ya taimaka gurin ceton MTN daga fatara
An bayyana a baya cewa Aisha Buhari wacce ta isa kasar Amurka a ranar 3 ga watan Augusta zata dauki tsawon kwanaki goma (10) a kasar.
Duk da haka, ta dawo gida Najeriya bayan tafiyar kwanaki hudu (4) kawai.
Matar Buhari ta samu tarba mai cike da karamci a filin jirgin saman Washington, tare da suka guda biyu na cewa batayi shiga ta musulunci ba kuma cewa jakar hannunta ta kai kimanin naira miliyan 34 (idan na ainahin ne) ko kuma dubu 120 (idan na jabbu ne).
The post Aisha Buhari ta gama ziyararta na kasar Amurka, zata dawo Najeriya (Hotuna) appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read Naij.com 24/7.