Babu maganar Biafra, Inji Shugaba Buhari
Babu maganar Biafra cewa Shugaban kasa Muhammadu Buhari.
Shugaba Buhari yace babu wata damar samar da wata Kasa Biafra daga Najeriya, Kungiyar IPOB dai ta dade tana ta fafutukar neman Kasa mai ‘Yanci watau Biafra daga Najeriya. Shugaba Buhari na Kasar yayi wannan jawabi ne daidai lokacin da ‘Yan Kungiyar ke zanga-zangar neman Kasar kan su-mai gashin kai. ‘Yan Yankin Kasar masu neman Kasar su ta kan su-Biafra sun nuna rashin amincewar su da Gwamnatin APC mai mulkin Kasar ne ta hanyar kin zuwa wuraren aiki na kwana guda.
KU KARANTA: Tofa. An kai Shugaba Buhari kotu
Shugaban Kasar Najeriyar wanda yana Kasar Amurka a lokacin wajen taron Majalisar dinkin Duniya ya bayyana hakan ta wata hira da ya zanta da manema labarai a Kasar. Shugaba Buhari yace maganar Biafra ma dai a bar ta, don ba za ta yiwu ba. Mutanen Biafra dai suna so suyi amfani da irin damar da Kasar Birtaniya ta samu ta fice daga Kungiyar EU ta nahiyar Turai, sai dai Shugaban Kasar Najeriyar ya nuna cewa babu yadda za ayi a samu wani yankin Biafra ya fice daga Kasar.
Sahara Reporters ta rahoto Shugaba Buhari na Kasar yana cewa idan abin da ya dace da mutanen yankin suyi shine, su kafa Jam’iyyar siyasa mai karfi har su samu Gwamnati, idan ya so sai su ci wa manufar su, da kuma Kasar Najeriya ta hanyar siyasa. Shugaban yayi wannan magana ne dai a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Amurka.
KU KARANTA: Tsagerun sun gargdadi Gwamnatin Buhari
Shugaba Buhari dai ya kuma bayyana irin nasarorin da ya samu a Taron da aka gabatar da Majalisar dinkin duniya watau UN. Femi Adesina ya fitar da wani jawabi, inda ya bayyana irin nasarorin da aka samu, musamman wajen harkar sauyin yanayi da yarjejeniyar Paris. Shugaba Buhari ya kuma samu damar yin magana da sauran Shugabannin duniya.
The post Babu maganar Biafra, Inji Shugaba Buhari appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read Naij.com 24/7.