Hukumar soji ta bayyana abinda ya faru tsakanin dakarun sojoji da yan Boko Haram
– Kanal Sani Kukasheka Usman ya gaya ma yan jarida abubuwa gaba daya wadanda sun auku inda dakarun sojoji sun fuskanta kungiyar yan ta’addan Boko Haram a jiya, Litinin 18, ga watan Afirilu
– Wani jami’i mai hudda da jama’a na hukumar sojin kasa ya bayyana wanda suke so farmaki wasu sojoji a garin Kareto dake jihar Borno a Arewa maso gabashin Najeriya
– Sojojin kasar Najeriya sun kashe yan ta’addan Boko Haram da yawa
Kungiyar yan ta’addan Boko Haram masu hallaka
Rahotanni na nuna cewa akan shafin Facebook din na jaridar Rariya, wanda inda aka kwana A Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Boko Haram.
KU KARANTA KUMA:
Idan ba a mance ba ‘yan Boko Haram sun kaiwa dakarun sojojin Nijeriya hari a garin Kareto dake Arewacin jihar Borno a safiyar yau. Saidai sojojin sun yi matukar yin nasara akan ‘yan bindigan, inda suka kashe da yawa daga cikin ‘yan ta’addan. Sannan kuma lamarin ya lafa.
Kanal Sani Usman Kukasheka, wani jami’i mai hudda da jama’a na hukumar sojin kasar Najeriya
Saidai wasu hafsoshin sojoji guda biyu da sojoji guda 22 sun samu rauni a yayin artabun. Dukkan sojojin suna asibitin sojoji, inda suke jinya. Sanarwar hakan ta fito ne daga bakin kakakin rundunar sojojin, Kanal Sani Kukasheka Usman.
The post Hukumar soji ta bayyana abinda ya faru tsakanin dakarun sojoji da yan Boko Haram appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read on NAIJ.COM.