An ga kwarangwal a dakin wani Fasto a Jihar Ogun
An ga wata kwarangwal a dakin wani faston addinin kirista a gidansa da ke Akute a jihar Ogun.
LIB ta bada rahoton cewa kwarangwal din wanda ake kyautata zaton na mace ne, an ga ta a ranan 14 ga watan Oktoba a dakin wani fasto a Peace land estate da ke Akute.
Mai gidan ya ga wannan abun al’ajavin ne yayinda yayi kokarin Koran faston daga gidansa akan rashin biyan kudin gida na tsawon shekara 1.
“Faston bai biya kudin wuta ba na shekara 1. Mai gidan ta ji haushi musamman yadda abubuwa sukayi wuya yanzu. Sai ta shiga gidan da wasu mutane domin fitar da shi. Shigansu ke da wuya sai suka ga abin tsoro,suka ga kwarangwal.”
A lokacin da mai gidan ta gani , sai ta kira makwabta da yan sanda. Amma faston wanda yake mai coci,yayi wadansu bayanai akan kwarangwal.
Yace na yar uwarsa ce. Iyayensu sun haifi yara 3 – shi da yan uwansa guda biyu. Yana zama da su a gidan amma bayan lokacin kadan,daya daga cikin yar uwar ta bace. Idan aka tambaye shi akan ta.sai yace ta tafi kan tsauni.
Ance ta mutu tun shekarar 2010 kuma aka bar gawar ta a cikin gidan. Da alamun cewa kwarankwak din na tsugunnu ne a kasa. Yan sanda sun tafi da faston.
The post An ga kwarangwal a dakin wani Fasto a Jihar Ogun appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read Naij.com 24/7.